Mai Magana da yawun dan takarar Gwamnan Kano a zaben 2019 da ya gabata, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a shafinsa na Facebook cewar, idan Allah ya basu nasara a zaben Gwamnan Kano a shekarar 2023, a cikin kwana darin farko zasu rushe duk wani gini da aka yi a filayen da basu kamata ba.
Bature ya kara da cewar, zasu cire dukkan sabbin Sarakunan da aka kirkiro a Kano, tare da dawo da Khalifa Muhammadu Sunusi II kan karagarsa a matsayin Sarkin Kano guda daya tilo.
Ya cigaba da cewar, kwana darin farko zasu kasance kwanakin Rusau ne a jihar Kano, inda zasu bi duk wani fili ko gini da aka yi a inda bai dace ba su rushe shi.
0 Comments